✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun tabbatar da kisan hakimi a Kano

Hakimin ya rasu a asibiti yayin da yake karbar kulawa daga likitoci.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da kisan gillar da aka yi wa hakimin kauyen Maigari, a Karamar Hukumar Rimin Gado da ke jihar.

An ruwaito cewar wasu ’yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka kashe Alhaji Dahiru Abbas mai shekara 70 a gidansa a ranar Lahadi.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

“A ranar Lahadi da misalin karfe 3:05 na safe ne aka samu rahoton cewa wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai farmaki gidan Abbas, Hakimin Maigari, a Karamar Hukumar Rimin Gado a kokarinsu na yin garkuwa da shi.

“Wadanda ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun harbi basaraken a kirji sannan an garzaya da shi Asibitin Kwararru na Murtala Muhammed da ke Kano inda a nan rai ya yi halinsa,” in ji shi.

Kiyawa ya kara da cewa an kara zage damtse domin kamo wadanda suka tafka aika-aikar.

Aminiya ta ruwaito cewa Maigari Abbas shi ne mahaifin Shugaban Karamar Hukumar Rimin Gado, Munir Dahiru Maigari.