✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yar Najeriya ta zama Birgediya -Janar a rundunar sojin Amurka

Ta fara aiki da rundunar ne tun a shekarar 1994

Wata sojar Amurka ’yar asalin Najeriya, Amanda Azubike, ta sami karin girma zuwa mukamin Birgediya-Janar a Rundunar Sojan Amurka.

Babban Kwamnandan Rundunar Sojin Kasa ta kasar, Manjo-Janar Antonio V. Munera, ne ya sanar da karin girman a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Alhamis.

“Muna taya murna ga sabuwar jami’ar da ta sami karin girma a Rundunar Sojan Kasa ta Amurka, Birgediya-Janar Amanda Azubike! A yau, ta sami karin girmanta daga Janar James Rainey, a yayin wani taro da ya sami halartar iyalai, abokai da sauran shugabannin al’umma,” kamar yadda ya wallafa a shafin nasa na Twitter.

An dai haifi Amanda ne a birnin Landan na Birtaniya, kuma iyayenta asalinsu ’yan Najeriya ne.

Ta fara aiki a matsayin sojar Amurka ne a shekarar 1994, sannan ta zama matukiyar jirgin saman rundunar, bayan ta kammala karatu a Makarantar da Horar da Direbobin Jirgin Sama ta Amurka.

Ta ci gaba da aiki a rundunar a matsayin jami’ar hulda da jama, bayan ta shafe shekara 11 a fagen tukin jirgin saman.

Yanzu haka, ita ce Mataimakiyar Kwamanda a Rundunar Sojin Kasa ta Amurkar, kuma a baya ta taba zama babbar jami’ar soja mai mai bayar da shawara a Ofishin Sakataren Tsaron Amurka.