’Yar margayi Sarki Fahd na kasar Saudiyya, Gimbiya Lolwah Bint Fahd Bin Abdulaziz Al Saud, ta riga mu gidan gaskiya.
A ranar Tatala, 19 ga watan Afrilu, 2022 za a gudanar da Sallar Jana’izar Gimbiya Lolwah, bayan Allah Ya yi mata rasuwa a ranar Litinin, wadda ta kasance 17 ga watan Ramadan din da muke ciki.
- Ranar 17 ga Ramadan aka yi Yakin Badar
- Yadda aka kama wasu barayin A Daitata Sahu a Kano
- An sanya na’urar fatawa da harshen Hausa a Masallacin Harami
Masarautar Saudiyya ta sanar cewa za a gudanar da sallar jana’izar marigayiyar a Masallacin Imam Turki Bin Abdullah da ke Riyadh, babban birnin kasar, bayan Sallar La’asar.
Tuni Sarakunan kasashen Larabawa da sauran sassan duniya suka shiga mika ta’ziyyarsu ga Sarki Salman na Saudiyya game da rashin Gimbiya Lolwah.
Sarkin Oman, Sultan Haitham Bin Tarik, ya mika sakon ta’aziyya ga Sarki Salman da iyalan gidan Sarautar Saudiyya, yana addu’ar samun rahama ga marigiyar da kuma juriya ga iyalan gidan.