Gwamnan ta bakin Shugaban Ma’aikatansa Sani Garba Shuni ya nemi mutanen Jihar Sakkwato su ci gaba da yin addu’ar samun zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.

A nasa bangare, Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ya ayyana hutun ne a ranar Alhamis, inda ya bukaci al’ummar Musulmi a jihar da su daga da addu’o’in samun karuwar arziki da zaman lafiya da kuma ganin bayan annobar coronavirus.