✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a fara biyan dalibai 38,183 tallafin karatu a Yobe

Kimanin dalibai 38,183 ne ake sa ran za su ci gajiyar tallafin.

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince a biya dalibai ’yan asalin Jihar da ke karatu a makarantun gaba da sakandaren kasar nan kudaden tallafin karo karatu.

Kimanin dalibai 38,183 ne ake sa ran za su ci gajiyar tallafin.

Bayanin hakan na kunshe ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin hukumar ba da tallafin karo karatun dake Damaturu, Tijjani Ciroma da ya aikewa manema labarai ranar Litinin.

A cewarsa, hukumar ta sanar da dukkan daliban dake karatu a jami’o’i da kwalejojin ilimi cewa gwamna Buni ya amince a biya su kudin tun a ranar takwas ga watan Oktoban 2021.

“Hukumar za ta yi zama da shugabannin daliban a mako mai zuwa don zayyana hanyoyin da za a bi wajen tantance daliban, sannan a tsara yadda za a fara biyansu kudaden,” inji sanarwar.

Daga nan hukumar ta ce za ta sanar da dukkan bangarorin dalibai da duk bayanan da suka dace kan tsare-tsaren nasu nan ba da jimawa ba.