✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a iya kawo karshen ’yan bindiga a wata 16 in aka ga dama – Fayemi

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya kuma Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce za a iya kawo karshen ’yan bindiga a wata 16 da suka rage…

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya kuma Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce za a iya kawo karshen ’yan bindiga a wata 16 da suka rage wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

Gwamnan na wadannan kalaman ne a wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Arise ranar Asabar, inda ya ce wurin da ’yan bindigar suke ba boyayye ba ne.

A cewar Gwamnan, jami’an tsaron sun san abin da za su yi su magance matsalar tsaron.

Ya ce muddin aka gaza kawo karshen matsalar a cikin lokacin, to tabbas akwai masu amfana da ita.

“Za mu iya gamawa da wadannan mutanen idan muka jingine batun hakkin bil Adama a gefe da zai iya zuwa daga kasashen waje. Ai su ba fatalwoyi ba ne.

“Mun san inda suke, za mu iya gamawa da su. Ba lallai ne gwamnati mai ci ta iya kammala aikin ba, amma za ta iya cin karfin matsalar.

“Sai dai idan akwai masu amfana da matsalar daga cikin jami’an tsaro, amma babu makawa za a iya murkushe su,” inji Fayemi.