✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a kwaso ‘yan Najeriya da suka makale a Saudiyya

Za a kwaso 'yan Najeriyar da suka makale a ranar 28 da kuma 29 ga Janairun 2021.

Gwamnatin Najeriya ta fara tattaunawar diflomasiyya tsakaninta da Gwamnatin Kasar Saudiyya don kwaso ‘yan Najeriya wadanda wa’adin takardun izinin zamansu a kasar ya kare.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha ne ya sanar da hakan cikin birnin Abuja a ranar Litinin yayin gabatar da jawaban karin haske dangane da halin annobar Coronavirus a kasar.

Ya ce, “Yanzu haka muna tattaunawa da masarautar kasar Saudiyya, don kwaso ‘yan Najeriya 600 da suka makale a kasar.”

Sanarwar da Sakataren Gwamnatin ya fitar ta bayyana cewa za a kwaso ‘yan Najeriyar cikin kwanaki biyu daga ranar 28 zuwa 29 ga Janairu.

Ya kara da cewa, da zarar sun dawo za a killace su na tsawon mako biyu kamar yadda ka’idodin dakile yaduwar cutar Coronavirus suka tanadar.

Kamfanin Dillacin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa, gwamnatin Saudiyya ta kama ‘yan Najeriyar ne wadanda wa’adin takardun izinin zamansu a kasar ya kare.