✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a raba wa manoma tallafin Naira biliyan 600

Manoma miliyan 2.4 za su amfana da rance mara ruwa, inji Buhari.

Gwamnatin Tarayya za ta raba wa namoma bashi mara ruwa na Naira biliyan 600 a yunkurinta na wadata kasa da abinci.

Shugaba Muhammadu Buhari ne ya sanar cewa manoma miliyan 2.4 ne za su amfana da rancen tallafin a fadin Najeriya karkashin shirin bunkasa samar da amfanin gona (APPEALS).

Ya ba da sanarwar ce a taron bikin baje kolin kayan goma da aka shirya domin bikin Ranar Abinci ta Duniya ta shekarar 2021 a Abuja.

Buhari ya yi bayanin ne ta bakin Ministan Noma da Raya Karkara, Mohammed Abubakar, wanda ya wakilce shi a taron wanda ya gudana a ranar Laraba.

Taken taron na bana shi ne “Ayyukanmu su ne rayuwarmu ta gaba: Samar da wadataccen abinci, Karin lafiyayyen abinci, muhalli da kuma rayuwa mai inganci”.

A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Harkokin Noma, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce gwamnatin Buhari ta jima tana bullo da manufofi da tsare-tsare domin samar da wadaccen abinci a Najeriya.