Hukumar da ke Kula da Matasa Masu yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) ta ce daga yanzu za ta hana duk matashin da bai yi rigakafin COVID-19 ba shiga sansanoninta na ba da horo.
Shugaban hukumar, Birgediya Janar Shu’aibu Ibrahim, wanda ya sanar da hakan ya ce matakin zai fara aiki ne lokacin da za a bude sansanin ba da horo na gaba a ’yan makonni masu zuwa.
- ’Yan bindiga sun kai hari kasuwar Taraba, sun yi awon gaba da mutum 3
- Tsananin yunwa ya fara kashe yara a Afghanistan
Ya ce daga yanzu, dole matasan su nuna shaidar rigakafin kafin a yi musu rajista a sansanonin hukumar.
Birgediya Janar Shuaibu ya ce hukumar na kokarin yin taka-tsan-tsan ne wajen ganin ba ta bar cutar ta dada yaduwa ba, musamman ma yanzu da samfurin Omicron ya bulla a Najeriya.
Sai dai ya ce daga yanzu ba za a sake ba matasan hutun mako biyu ba bayan kammala karbar horo a sansanoni, inda ya shawaresu da su koyi sana’a ba tare da sun dogara da ayyukan gwamnati ba.
Ya kuma gargadi matasan da su kiyayi tafiye-tafiye da daddare, saboda kalubalen tsaro.
“Muna da dakunan kwanan matasa masu yi wa kasa hidima da sakatariya a kowacce jiha da barikokin sojoji, kamata ya yi ku tsaya ku kwana a can in kuka yi dare, kashegari ku ci gaba da tafiya,” inji Shugaban na NYSC.