✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Za mu sa jirage marasa matuka a yaki da ’yan bindiga’

Za kuma a karo jirage takwas da masu saukar ungulu domin murkushe 'yan bindiga

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya za ta yi amfani da jirage marasa matuka wurin yakar ’yan bindiga a yankin Arewa ta Yamma da ta tsakiya. 

Shugaban Rundunar, Air Marshal Sadique Abubakar ya ce na gaba za a tura jirage marasa matuka guda takwas jihohin Zamfara Katsina da Gombe da ’yan bindiga ke addaba.

A ziyararsa ta ganin irin nasarar da ake samu a yaki da mahara a Jihar Katsina, Air Mashal Sadique ya ce dakarun rundunar guda 71 da za su rika kula da jiragen da ke samun horo a China na gab da dawowa gida.

Ya kara da cewa Gwamnatin Tarayya za ta karo jirage takwas da masu saukar ungulu da karin kayan yaki domin murkushe ayyukan mahara a yankin.

Shugaban Rundunar ya shaida wa ’yan jarida cewa an yi nasarar ragargaza sansanonin bata-garin a Jihohin Katsina, Zamfara, Neja da kuma Sakkwato.

Ya ce gwamnati ta dukufa wajen ganin an samu aminci a yankunan da ke fama da matsalar tsaro a yankin.

Sadique ya ce ba za su kakkauta ba wajen ragargazar mahara da sauran masu aikata manyan laifuka ba saboda a yi saurin kawar da ayyukansu.