✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za mu yi amfani da bindiga a zaben cike gurbi —’Yan sanda

Domin kawo tsaro da magance tashin-tashina 'yan sanda zasu yi amfani da bindigogi a cewar Kwamishinan 'yan sandan jihar.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Filato Edward Ebuka, ya ce wasu jami’an runudunar za su yi amfani da bindiga don dakile tarzoma a zaben cike gurbi da za a yi a jihar.

Za a yi zaben kujerar Sanatan Filato ta Kudu ne a ranar Asabar 5 ga Disamba, 2020, domin cike gurbin Ignatius Longjan da ya rasu a 2019.

Kwamishinan ya samu wakilcin Yinusa Ishak, a taron masu ruwa da tsaki da Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta shirya.

Ishak ya ce rundunar ba za ta rika zura ido bata-gari na cin karensu ba babbaka a lokacin zabe ba.

Ya ce Kwamishinan ’yan sandan jihar ya ce babu wanda za a bari ya kada kuri’a ba tare da ya sanya takunkumi ba.

Sannan ya ce dole ne mutum ya bude fuskarsa kafin kada kuri’a saboda gudun kada wani ya jefa kuri’a a madadin wani.

Ya kuma jaddada cewa dole ne a bi matakan kariyar cutar COVID-19 don kauce wa yaduwarta.

Jami’in ya ce duk wanda aka samu da alamar cutar za a dauke shi zuwa inda za a ba shi agajin gaggawa.