✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaben dan takarar PDP: Wike ya maka Atiku da Tambuwal a kotu

Ana zargin Wike na shirin sauya sheka daga PDP

Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, ya maka dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal da kuma ita kanta jam’iyyar a kotu.

Wannan na zuwa ne baya zaben fidda-gwani da aka gudanar a Abuja, inda Tamnuwal a lokacin da yake jawabi ga wakilan jam’iyyar da su zabe shi, amma daga bisani ya janye wa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku, takararsa.

A zaben fidda-gwanin Atiku ya samu kuri’u 371 wanda hakan ya sa ya yi nasara, yayin da Wike ya samu 237 a matsayin na biyu.

Tun bayan kammala zaben fidda-gwani na PDP ne dai Wike da magoya bayansa ke takun-saka da magoya bayan Atiku.

Bayan da aka dauki tsawon lokaci ana rikicin jam’iyyar, Wike da wani jigo a PDP, Newgent Ekamon a yanzu sun maka Atiku, Tambuwal da PDP kara a kotu, tare da mika sammaci mai lamba FHC/ABJ/CS/782/2022, ga wadanda ake kara.

A sammacin, an sanya PDP a matsayin wanda ake kara ta farko, sai Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) a matsayi wadda ake kara ta biyu, Tambuwal da Atiku a matsayin na uku da na hudu.

Daga cikin batutuwan da aka lissafo, Wike da Ekamon sun nemi kotun da ta umarci INEC da ta hana Atiku takara a zaben shugaban kasa na 2023.

Tuni aka fara rade-radin cewa Gwamna Wike na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP.

Wasu rahotanni sun ce an cire tutocin ofishin Jam’iyyar PDP a Jihar Ribas, lamarin da ya haifar da yamutsi aka shiga tunanin ko maganar shirye-shiryen ficewar Wike daga PDP na dab da faruwa.