✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaben fitar da gwanin APC: Fastotin ’yan takara sun yi wa filin zabe tsinke

Fastocin dai na ta kokarin daukar hankalin masu wucewa

Yayin da dandalin Eagle Square, wajen da za a gudanar da zaben fitar da gwanin dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 ya fara daukar harami, fastocin masu neman takarar sun mamaye kowane kungu da sako na filin.

’Yan Najeriya dai na jiran daliget din jam’iyyar da za su zaba mata wanda zai yi mata takarar, domin fafatawa da dan takarar PDP, Alhaji Atiku Abubakar.

Fastocin dai na ta kokarin daukar hankalin masu wucewa zuwa wuraren ayyukansu.

Ga wasu daga cikin fastocin ’yan takarar da muka kalato muku daga wajen: