✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaben Ondo: Akeredolu ya dauko hanyar nasara

Sakamakon zaben Gwamnan Jihar Ondo ya nuna Rotimi Akeredolu yana kan gaba.

Sakamakon zaben Gwamnan Jihar Ondo ya nuna Rotimi Akeredolu yana kan gaba a kananan hukumomi 12 cikin 15 da aka bayyana sakamakonsu.

Ya samu jimillar kuri’u 219,219 ga APC, yayin da abokin hamayyarsa Eyitayo Jegede na PDP ya samu 170,498.

Ya zuwa yanzu dan takarar jam’iyyar ZLP (Zenith Labour Party), Agboola Ajayi, shi ne a matsayi na uku shi ne inda ya samu kuri’u 53,422.

An dakatar da sanar da sakamakon zaben a ranar Asabar bayan da aka bayyana sakamakon kananan hukumomi 12.

Da misalin karfe 9 na safiyar ranar Lahadi, an ci gaba da bayyana sakamakon inda Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta gabatar da na kananan hukumomi uku.

Ga dai sakamakon kananan hukumomi da ya zuwa yanzu Hukumar Zabe ta kasa ta fitar kamar haka:

Ose

APC: 15,122

PDP: 8,421

ZLP: 1083

Okitipupa

APC: 19,266

PDP: 10,367

ZLP: 10,120

Owo

APC: 35,957

PDP: 5,311

ZLP: 408

Ondo ta Gabas

APC: 6,486

PDP: 4,049

ZLP: 3,221

Akoko Ta Arewa maso Yamma

APC: 15,806

PDP:10,320

Akoko Ta Kudu maso Yamma

APC: 21,322

PDP:15,055

Akoko Ta Arewa maso Gabas

APC: 16,572

PDP: 8,380

Irele

APC: 12,643

PDP: 5,493

Ile Oluji

APC: 13,278

PDP: 9,231

ZLP: 1,971

Ifedore

APC:9,350

PDP:11,852

Akure Ta Arewa

APC: 9,546

PDP: 12,263

ZLP: 1,046

Idanre

APC: 11,286

PDP: 7,499

ZLP: 3,623

Ondo Ta Yamma:

APC: 15,977

PDP: 10,627

ZLP: 10,159

Odigbo

APC: 23,571

PDP: 9,485

ZLP: 6,540