✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaftarewar kasa ta kashe mutum 18 a Brazil

Zaftarewar kasa da ambaliya a sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya ya haddasa mutuwar mutum 18 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil.

Zaftarewar kasa da ambaliya a sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya ya haddasa mutuwar mutum 18 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil.

Ma’aikatan kashe gobara ta kasar Brazil ta tabbatar da mutuwar mutum 18 sakamakon ifti’ain, amma ba ta bayar da alkaluman wadanda suka jikkata ko suka bata ba.

Lamarin ya faru ne a a wani yanki da masu yawon bude ido ke yawan ziyarta a tsaunukan birnin Rio.

Ma’aikatar ta ce ma’aikatan kashe gobara 180 da sauran ma’aikatan ceto ne ke aikin ceto a wurin da abin ya faru a tsaunukan Petropolis, inda aka binne sarkin Brazil na karshe Pedro II, mai tazarar kilomita 68 daga arewacin birnin Rio.

“An aike da tawaga ta musamman da motoci da jiragen ruwa domin gudanar da bincike da ceto mutanee,” inji sanarwar.

Majalisar birnin ta ayyana “dokar ta-baci” a yayin da aka yada hotuna gidaje da motocin da suka lalace a sakamakon ibtila’in.

Shaguna da dama sun cika makil da ruwa sakamakon ambaliyar da ta shafe titunan tsakiyar birnin Rio mai dimbin tarihi.