✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zan koma gona bayan karewar wa’adin mulkin Buhari — Femi Adesina

Ya ce zai koma gona gadan-gadan a 2023

Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, ya ce zai koma gona gadan-gadan da zarar wa’adin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kare a 2023.

Ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Alhamis, lokacin da ya karbi bakuncin Kungiyar Manoma ta Kasa (AFAN), reshen Jihar Edo a ofishinsa.

A cewarsa, “Idan wa’adin gwamnatinmu ya kare a 2023, da yardar Allah ina da shirin komawa aikin jarida ka’in da na’in da kuma gona. Allah Ya taimaka mana Amin.

“Abin alfahari ne sosai lokacin da aka shaida min cewa za ku ziyarce ni don nada ni a matsayin uban kungiya.

“Na yi mamaki sosai sannan na tambayi kaina, ta yaya suka san ina da shirin komawa gona? Kamar suna duba?,” kamar yadda Femi Adesina ya wallafa.

Kakakin Shugaban Kasar dai ya yi aiki a gidajen jarida Vanguard da kuma National Concord, da kuma The Sun, har zuwa shekarar 2015 lokacin da ya ajiye matsayi Babban Editanta don fara aiki a gwamnatin Buhari.