✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zan tsaya takarar Gwamnan Kaduna – Sanata Uba Sani

Sanatan ya ce yana so gaji El-rufa'i a Jihar a 2023

Sanata mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattijai, Uba Sani, ya bayya aniyarsa ta tsayawa takarar Gwamnan Jihar Kaduna a zaben 2023.

Ya bayyana hakan ne a wajen taron jam’iyyar APC na Jihar, a ranar Talata.

Sanatan ya ce ya ziyarci sakatariyar jam’iyyar ne don neman hadin kai da goyon baya.

“Na zo na sanar da ku aniyata ta tsayawa takarar Gwamna a APC. Ina bukatar goyon bayanku da tallafinku,” in ji shi.

Kazalika, Sanatan ya jinjina wa Gwamnan Jihar mai ci, Nasir El-Rufa’i kan yadda ya ce ya ciyar da Jihar gaba.

Gwamnan dai yayin wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a kwanakin baya, ya bayyana cewar wanda zai zama Gwamnan Jihar a 2023 na daga cikin jerin mutanensa na kusa-kusa.

“Abin da nake nufi na kusa-kusa, su ne wanda suka yi aiki kafada da kafada da ni tun 2014 wajen hada kan jam’iyya, har zuwa lokacin da muka ci zabe,” inji El-Rufa’i.

Uba Sani dai na daga cikin mutum 11 ’yan gaba-gaban El-Rufa’i, wanda ya faro daga matakin mai bai wa Gwamnan shawara tun daga 2015 zuwa 2019, kafin daga bisani ya sauka ya yi takarar kujerar Sanata.