Kotun Kula Ma’akata ta Kasa ta dakatar da Gwamnatin Jihar Kano karkashin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje daga korar Barista Muhyi Magaji Rimingado daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Karbar Korafe-korafe da Yaki da Rashawa ta jihar.
Wannan ya biyo bayan rokon da lauyoyin Barista Muhuyi Magaji Rimingado suka gabatar a gaban kotun da ke zamanta a Kano, a shari’ar da yake kalubalantar korar da gwamnatin Kano ta yi masa, wadda ya ce ta saba doka.
A zaman kotun na ranar Litinin Lauyan Muhyi, Barista Yusuf Ali Faragai, ya bayyana wa kotun cewa takardar da Gwamnatin Jihar Kano ta bayar a matsayin ta korar wanda yake karewa, a fahimtarsu an yi ta ne ba bisa ka’ida ba.
Faragai ya kara da cewa, tuni suka shigar da kara a Birnin Tarayya Abuja kuma kotu ta tabbatar da Barista Muhuyi Magaji Rimingado a matsayin halastaccen Shugaban Hukumar Karbar Qorafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano.