✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An gano gawar shugaban Fulani a rijiya a Filato 

Muna kira ga daukacin mambobinmu da su kwantar da hankalinsu, kada su dauki doka a hannunsu.

An gano gawar wani shugaban Fulani da ya bace, Umar Ibrahim, a wata rijiya a unguwar Jokom da ke garin Mangu na Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Marigayi Ibrahim shi ne Ciroma na gundumar Kumbun a Karamar Hukumar Mangu.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ (OPSH) da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a jihar, Kyaftin Oya James, ya tabbatar da faruwar lamarin.

A halin da ake ciki, shugaban kungiyar Gan Allah Fulani (GAFDAN), ya bayyana cewa Ibrahim ya bace ne lokacin da ya fito daga asibiti a ranar Laraba don siyo wa matarsa abinci da ke garin Mangu amma bai dawo ba sai da yammacin ranar Lahadi da aka tsinto gawarsa a cikin rijiyar.

Shugaban kungiyar na jihar, Garba Abdullahi ya ce, “Ya ziyarci matarsa da ba ta lafiya da ke Mangu.

“Ranar Laraba misalin karfe 6 na yamma ya fita ya siyo mata abinci amma bai dawo ba.

“Bayan an shafe kwanaki hudu ana nemansa, an tsinci gawarsa a wata rijiya a kusa da asibitin.

“An tsinto gawar ce a gaban sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke tabbatar da zaman lafiya a yankin.

“Sai dai duk da faruwar wannan lamari muna kira ga daukacin mambobinmu da su kwantar da hankalinsu, kada su dauki doka a hannunsu.

“Ya kamata mu ci gaba da zama masu bin doka. Hukumomin tsaro suna yin iya kokarinsu.

“Kiranmu ga jami’an tsaro shi ne kawai su kamo wadanda suka aikata wannan ta’asa domin a hukunta su.”