Baraken yankin Aghara da ke Karamar Hukumar Kabba-Bunu a Jihar Kogi State, Cid David Obadofin ya rasu a hannun ’yan bindiga, kwana 12 bayan sun yi garkuwa da shi.
Wani daga cikin iyalan basaraken ya shaida wa Aminiya cewa ya rasu ne sakamakon azabtarwar da ’yan bindigar suka yi masa.
Aminiya ta gano cewa ’yan bindigr sun amince su sako basaraken tare da wata mata a kan kudin fansa Naira miliyan biyu, bayan da suka lura cewa ya riga ya galaba ita.
Sai dai kafin a kai ga mika musu kudin fansnan suka rufe idon matar suka sauya mata wuri,