✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda ake tsangwamar Fulani a sansanin gudun hijira

Fulani ’yan gudun hirija na tsoron wasu kabilu za us kai musu hari a sansanin gudun hijira.

Fulani ’yan gudun hirija suna cikin tsaka mai wuya inda suke fuskantar tsangwama a Kananan Hukumomin Munya da Shiroro na Jihar Neja.

Daruruwan Fulani ’yan gudu hijira, yawancinsu mata da kananan yara na zaune cikin zullumi saboda tsoron wasu kabilu da ke kai farmaki a kauyukan Fulani za su kai musu hari.

Hakan na zuwa ne bayan hare-haren ’yan bindiga sun tilasta wa akalla mutum 5,000 daga kauyuka daban-baban neman mafaka a Fadar Sarkin Minna, inda daga baya aka yi musu matsuguni a makarantar firamaren IBB da ke garin Minna.

Sai dai tsoron wasu kabilu za su kai musu hari, ya sa Fulani ’yan gudun hijira neman mafaka a wasu wuraren.

Aminiya ta gano wasu ’yan gudun hijirar na barin sansanin; wasunsu na komawa wurin ’yan uwansu a wasu kauyuka, zuwa lokacin da al’amura za su daidaita.

Hukumar Bayar da Agaji ta Jihar Neja (NSEMA) ta ce tana zagayawa a garin Minna domin daukar bayanan ’yan gudun hijirar da ke zaune a gidajen al’umma.

Darakta-Janar na Hukumar, Ibrahim Inga, ya ce akalla gidaje hudu ne suka saukar da masu gudun hijira a garin.

Ya ce wuraren su ne: Three arm zone, mutum 248; Bayan Dana, 68; FM Junction, 48; Angwan Daaji, 59

An kuma gano cewa Hukumar na shirin mayar wa wasu Fulani ’yan gudun hijirar zuwa sansanin ’yan gudun hijira da ke Sarkin Pawa.

A lokacin da ya ziyarci sansanin ’yan gudn hijirar da ke Minna, Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya zargi Gwamnatin Tarayya da yin shakulatun-bangaro da halin da mutanen suke ciki.