✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fuskokin Limaman Sallar Tarawih da Tahajjud a Makkah

Manyan limamai da aka zabo don jagorantar sallolin dare a watan Ramadan, 2021

Hukumomin Saudiyya sun fitar da jerin sunayen limaman da za su jagoranci Sallolin Taraweeh da na Tahajjud a Masallaci mai alfarma na birnin Makkah a cikin watan Azumin Ramalana mai kamawa.

Shafin intanet na Haramain Sharidain ya sanar cewar limamai shida ne za su jagorancin sallolin a tsawon watan Azumin bana, karkashin jagorancin Sheikh Abdurrahman As Sudais, Babban Limamin Masallatai biyu mafiya alfarma a doron kasa na Makkah da Madinah.

Limaman su ne Sauran su ne;

  1. Sheikh Saud Al Shuraim
  2. Sheikh Abdullah Awad Al Juhany
  3. Sheikh Maher Al Muaiqly
  4. Sheikh Bandar Baleelah da kuma
  5. Sheikh Yasir Al Dossary.
Sheikh Saud Al Shuraim
Sheikh Yasir Al Dossary
Sheikh Maher Al Muaiqly
Sheikh Bandar Baleelah
Sheikh Abdullah Awad Al Juhany
Sheikh Abdurrahman As Sudais

Kazalika, sanarwar ta ce a bana babu wani limami daga wani masallaci da za a gayyato domin jagorantar sallolin.