✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kenya ta dawo da tallafin mai bayan fuskantar matsin lambar jama’a

Kasar ta ce za ta ci gaba da biyan tallafin na wata daya

Gwamnatin kasar Kenya ta ba da kai boyi ya hau wajen sake mayar da tallafin man da ta janye bayan jama’ar kasar sun tayar da kayar baya kan tsadar rayuwa a kasar.

Gwamnatin dai ta ce za ta ci gaba da biyan tallafin ne har na tsawon kwanaki 30 masu zuwa.

Tun lokacin da aka rantsar da shi a matsayin Shugaban Kasar a watan satumbar bara, William Ruto ya janye tallafin da ake biya a man fetur da masara da fulawa, wadanda ya gada daga wanda ya karbi mulki a hannunsa.

Shugaban dai a wancan lokacin ya ce ya gwammace ya bayar da tallafi a bangaren masana’antu ba wai a fannin abubuwan da ake amfani da su na kai tsaye ba.

Ya kuma ce an dauki matakin ne da nufin rage yawan kudaden da gwamnatin ke kashewa a daidai lokacin da kasar ke fafutukar biyan basussukan da suka yi mata katutu.

Sai dai janye tallafin da kuma kara harajin da gwamnatin kasar ta yi a ’yan kwanakin nan ya dada ta’azzara tsadar rayuwa a kasar, wacce kuma ta sanya jama’a yin zanga-zangar neman sassauci daga gwamnati.

A cewar Kamfanin mai na kasar, gwamnati ta kuma sanya dan kwarya-kwaryar tallafi a kan kananzir da man dizel.

Farashin man fetru dai ya yi tashin gwauron zabi bayan Shugaba Ruto ya janye tallafi. Ya kuma dada tashi a watan Yuli bayan gwamnatin ta kara kudaden harajin man da sauran kayayyakin makamasji a kasar.