Wata kotun shari’ar musulunci da ke zaune a a Karamar Hukumar Fagge ta Jihar Kano, ta ba da umarnin tsare wani mai suna Umar a gidan kaso, bisa tuhumarsa da laifin satar takalma.
Aminiya ta ruwaito cewa, ana zargin matashin da satar takalma har kafa 21 wanda darajarsu ta kai kimanin Naira dubu 243.
- Dukan da ’yan bindiga suka yi wa fasinjojin jirgin kasa somin tabi ne —Kubutaccen Fasinja
- GANI YA KORI JI: Hotunan zanga-zangar Kungiyar Kwadago kan yajin aikin ASUU
‘Yan sanda ne dai suka gabatar da karar a gaban kotun kan wanda ake zargin da ke zaune a unguwar Kofar Ruwa.
Sai dai Umar ya musanta zargin da ake masa, lamarin da ya sanya Alkalin kotun, Isma’il Muhammad Ahmad ya dage zaman zuwa 9 ga watan Agusta .
Tun da fari dai, dan sanda mai gabatar da kara, Abdul Wada, ya sanar da kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin ne a ranar 22 ga watan Yuli a Unguwar Goron Dutse.
“Da misalin karfe 3 na ranar 22 ga watan Yuli ne, wanda ake zargin ya balle shagon wani mai suna Sani Abubakar kuma ya saci takalma kafa 21,” a cewar Wada.
Dan sandan ya kuma sanar da kotun cewa lokacin da wanda ake zargin ya shiga hannu, an samu takalma kafa shida a hannunsa.
Laifukan a cewarsa, sun saba wa sashi na 133 na kundin dokar kotun.