✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kwamandan ’yan bindiga Daudawa ya mika wuya a Zamfara

Mun rantse da Alkur'ani ba za mu sake komawa ta'addanci ba.

Wasu ’yan bindiga guda shida karkashin jagorancin shugabansu, Auwalu Daudawa sun mika wuya tare da sallama wa gwamnatin Jihar Zamfara bindigogi 28 kirar AK-47 a ranar Litinin.

Kimanin kwanaki goma da suka gabata ne wasu ’yan bindiga shida suka tuba tare da mika wa hukumomin Jihar bindigogi 14 suna masu alkawarin watsar da ayyukan ’yan bindiga da sauran ababe na ta’ada.

Wadanda aka karbi tubansu a fadar Gwamnatin Jihar da ke birnin Gusau, sun yi rantsuwa da Alkur’ani cewa ba za su sake komawa wannan mummunar ta’ada ba.

Kazalika, jagoransu Auwalu Daudawa ya yi alkawarin janyo ra’ayin wadanda har yanzu suke rike da makamai domin su tuba.

Da yake karbar mutanen da suka tuba, Gwamna Bello Matawalle ya kirayi dukkan ’yan bindigar da su fito su amince da tsarin sulhu da gwamnatinsa ta kirkiro inda ya yi alkawarin kula da duk wadanda suka tuba.

“Gwamnatina za ta kula da duk ’yan bindigar da suka tuba sannan zan ci gaba da tattaunawa da su domin kawo karshen ta’addanci a Jihar,” in ji Matawalle.

Matawalle ya yi kira ga mutanen jihar, musaman ’yan siyasa da su bai wa gwamnatinsa goyon baya a kokarinta na kawar da masu satar mutane da sauran ababe na ta’ada.