✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Majalisa ta bukaci CBN ya dakatar da shirin takaita hada-hada da tsabar kudi 

Majalisar ta bukaci a dakatar da shirin saboda bukatar jama'a

Majalisar Dattijai a ranar Laraba ta bukaci Babban Bankin Najeriya (CBN) da ya dakatar da shirinsa na takaita adadin tsabar kudaden da za a iya cira a kullum.

A makon da ya gabata ne dai babban bankin ya ce daga ranar tara ga watan Janairu mai zuwa za a takaita yawan kudaden da mutum zai cira zuwa N100,000 a kullum, sai kuma N500,000 ga kamfanoni.

Amma majalisar, bayan yin nazari kan rahoton kwamitinta na Harkokin Banki, ta bukaci CBN da ta jinkirta dokar saboda korafe-korafen jama’a.

Majalisar ta kuma bukaci kwamitin nata da ya sa ido yadda ya kamata a kan ayyukan bankin, sannan ya zo mata da rahoto.

Muna tafe da karin bayani…