✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Majalisa ta tantance Festus Keyamo bayan ya bayar da hakuri

An fargar da majalisar a kan yadda a baya Keyamo ya nuna rashin da’a ga majalisa ta 9.

Majalisar Dattawa ta tantance Festus Keyamo daga Jihar Delta a matsayin minista bayan dambarwar da ta mamaye tantacewar farko.

Festus Keyamo ya bayar da hakuri a kan kuskurensa na baya, inda ya ki amsa gayyatar majalisa ta 9 kan ayyukansa a matsayin Karamin Ministan Kwadago.

A lokacin zaman tantancewar, Sanata Darlington Nwokocha daga Jihar Abiya ya fargar da majalisar a kan yadda a baya Keyamo ya nuna “rashin da’a” ga majalisa ta 9, inda ya zargi majalisar da aikata rashawa.

Tsohon Ministan Kwadagon ya bayar da hakuri sannan ya yi karin haske kan abubuwan da suka faru a wancan lokacin.

Da farko dai Sanata Darlington ya nemi a dakatar da tantance Keyamo, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce har ya kai ga tsaiko ga aikin tantancewar.

Daga baya dai majalisar ta dawo ta kuma yafe masa laifin da ya yi a baya.

Festus Keyamo ne mutum na karshe da majalisar ta tantance daga cikin 48 da Shugaba Bola Tinubu ya aike mata don amincewa da su a matsayin ministoci.

Festus Keyamo shi ne ministan gwamnatin Buhari da ya sake shiga cikin jerin sunayen wadanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai nada a matsayin minista

Kawo yanzu bayan shafe kwanaki takwas ana aikin majalisar ta tantance mutum 45 kamar yadda Shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya sanar.

Ragowar ukun da majalisar ta tantance amma ake jiran a tabbatar da su ta fuskar tsaro sun hada da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai da Abubakar Sani Danladi daga Jihar Taraba da kuma Stella Okotete daga Jihar Delta.

Wadanda aka kammala tantacewa sun hada da:

Akwa Ibom: Ekperikpe Ekpo

Bayelsa: Heineken Lolokpobri

Kuros Riba: Betta Edu

Kuros Riba: John Enoh

Edo: Abubakar Momoh

Ribas: Nyesom Wike

Adamawa: Tahir Mamman

Bauchi: Yusuf Maitama Tuggar

Bauchi: Ali Pate

Borno: Abubakar Kyari

Gombe: Alkali Ahmed Saidu

Taraba: Uba Maigari Ahmadu

Yobe: Ibrahim Geidam

Jigawa: Mohamed Badaru

Kano: Mariya Mahmoud Bunkure

Kano: Abdullahi T. Gwarzo

Katsina: Ahmad Dangiwa

Katsina: Hannatu Musawa

Kebbi: Yusuf Tanko Sununu

Kebbi: Atiku Bagudu

Sakkwato: Bello M. Goronyo

Zamfara: Bello Matawalle

Abia: Nkiruka Onyejiocha

Anambra: Uju Ohaneye

Ebonyi: David Umahi

Enugu: Uche Nnaji

Imo: Doris Uzoka

Ekiti: Dele Alake

Legas: Tunji Alausa

Legas: Lola Ade-John

Ogun: Isiak Salako

Ogun: Bosun Tijjani

Ogun: Olawale Edun

Ondo: Olubunmi Tunji-Ojo

Osun: Adegboyega Oyetola

Oyo: Adebayo Adelabu

Benuwe: Joseph Utsev

Abuja: Zaphaniah Bitrus Jisalo

Kogi: Shuaibu A. Audu

Kwara: Lateef Fagbemi

Nasarawa: Imaan S. Ibrahim

Neja: Mohammed Idris

Neja: Aliyu Sabi Abdullahi

Filato: Simon Lalong

Delta: Festus Keyamo