✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masu garkuwa da dan Majalisar Taraba na neman miliyan N150

Masu garkuwar sun dage cewa dole sai an ba su kudaden da suka bukata

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da dan Majalisar Dokokin Jihar Taraba sun nemi a biya su kudin fansa Naira miliyan 150.

Masu garkuwar sun tuntubi iyalan Bashir Muhammad mai wakiltar Mazabar Nguroje a yankin Sardauna wanda suka sace a gidansa a Jalingo a daren Alhamis.

Majiyarmu ta ce ana kan tattauanwa tsakanin dangin Bashir Muhammed da masu garkuwa da mutanen.

Majiyar ta ce ’yan bindigar sun dage cewa dole sai an ba su kudin da suka nema kafin su sako shi.

Bashir Muhammed wanda ke cikin firgici ya roki shugabannin majalisar dokoki kuma gwamnatin jihar ta Taraba da su taimaka su biya bukatun masu garkuwar domin ceto rayuwarsa.

Tuni dai ’yan majalisar dokokin jihar, a cewar wata majiya ta gana da Gwamna Darius Ishaku kan batun.