✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutane sun je kona cibiyar allurar rigakafin COVID-19

Ana neman wadanda suka kai wa cibiyar hari da abubuwan fashewa.

Jami’an tsaro na neman wasu mutane da suka kai hari da nufin kona wata cibiyar bayar da allurar rigakafin cutar COVID-19.

Akalla mutum uku ne jami’an tsaron suke name kan yunkurin na kona cibiyar allurar rigakafin COVID-19 din da ke Jihar Saxony ta kasar Jamus.

Ana zargin wasu mutum uku ne suka jefa kwalabe cike da makamashi a cikin ginin cibiyar allurar rigakafin cutar a garin Treuen da yammacin ranar Talata.

Wasu shaidu sun ce maharan sun kai wa cibiyar farmaki ne a cikin wata jar mota, amma har yanzu ba a ga alamar motar ba.

Mai magana da yawun ’yan sanda a garin ya ce karon farko ke nan da aka kai irin harin a a garin.

Sai dai ya bayyana cewa abin ya zo da sauki saboda bai yi barna ba sosai a cibiyar, hasali ma abubuwan fashewar ba su tashi ba.

A karshen watan Satumban da muke ciki ne ake sa ran rufe cibiyar da aka kai wa harin, tare da wasu cibiyoyin rigakafin 12 da ke Jihar ta Saxony