✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tabbas an yi wa shafinmu kutse —EFCC

EFCC ta kawo karshen harin da masu kutse suka kai wa shafinta na intanet

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC) ta tabbatar da cewa wasu da da ta kai ga sanin ko su wane ne ba sun yi kutse a shafinta na intanet a karshen makon jiya.

Mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren ya tabbatar da haka, amma ya ce an yi nasarar magance matsalar a kan kari.

“Duk da cewa an yi kokarin yi wa shafin mu kutse a karshen makon jiya, an dakile harin kuma yanzu shafin na aiki yadda ya kamata”, inji wani sako da ya wallafa ta Twitter.

Idan ba a manta ba a ranar Juma’ar da ta gabata ne wasu da masu fafutkika masu taken ‘Babu wanda ya san mu’, a cikin wasu jerin sakonnin da suka fitar ta intanet suka ce sun yi kutse a shafukan wasu hukumomin Gwamnatin Tarayya domin goyon bayan masu zanga-zangar #EndSARS da ke gudana a kasar.

Hukumomin da suka ce sun yi wa kutse su ne EFCC, Babban Bankin Najeriya (CBN), Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da sauransu.

A lokacin da wakilinmu ya yi kokarin shiga shafin EFCC a ranar Juma’a sai ya samu sakon cewa shafin na da matsala.

Idan ba a manta ba maharan sun yi kutse a shafin Twitter na Hukumar Kula da Kafafen Watsa Labarai, inda suka wallafa sakon goyon bayan zanga-zangar #EndSARS.