Wani matashi da ya kware a satar mota ya shiga hannun jami’an ‘yan sandan Jihar Katsina.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Katsina SP Gambo Isa, ya ce Shu’ aibu Mohammad ya dade yana amfani da irin makullin nan na musamman da ake kira ‘masta ki’. Ya fada hannun jami’an ne bayan satar wata mota kirar Golf.
Ba wannan ne karon farko da aka tava kama wannan matashin ba.
Karin bayani na nan tafe kadan, domin jami’an na ci gaba da bincike.