Dan takarar gwamnan Jihar Kano karkashin jam’iyyar PDP a zaben shekarar 2011 da 2015, Malam Salihu Sagir Takai ya kaddamar da kwamitin mutum 15 don jagorantar kamfe dinsa a zaben shekarar 2019.
Kwamitin wanda babban kwamitin gudanarwar takarar Takai a zaben 2019 ya kaddamar jiya, Takai da kansa ne zai jagoranci kwamitin.
A wata sanarwa da Barista Faruk Iya Sambo ya sanya wa hannu ta nuna cewa an dorawa kwamitin alhakin shirya kamfe din takarar Takai a zaben shekarar 2019 karkashin kwamitin gudarwa.