✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Takarar gwamnan Kano: Takai ya kaddamar da kwamitin mutum 15

  Dan takarar gwamnan Jihar Kano karkashin jam’iyyar PDP a zaben shekarar 2011 da 2015, Malam Salihu Sagir Takai ya kaddamar da kwamitin mutum 15…

 
Dan takarar gwamnan Jihar Kano karkashin jam’iyyar PDP a zaben shekarar 2011 da 2015, Malam Salihu Sagir Takai ya kaddamar da kwamitin mutum 15 don jagorantar kamfe dinsa a zaben shekarar 2019.
 
Kwamitin wanda babban kwamitin gudanarwar takarar Takai a zaben 2019 ya kaddamar jiya, Takai da kansa ne zai jagoranci kwamitin.
 
A wata sanarwa da Barista Faruk Iya Sambo ya sanya wa hannu ta nuna cewa an dorawa kwamitin alhakin shirya kamfe din takarar Takai a zaben shekarar 2019 karkashin kwamitin gudarwa.