✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Taraba: ’Yan bindiga sun kashe mutum 4, sun sace mai gari da matansa

Maharan sun sace mai gari da matansa biyu a dare guda.

’Yan bindiga sun kashe mutum hudu, suka sace wasu hudu, ciki har da Mai Garin Maigemu da matansa biyu a kauyukan Maigemu da Kwantan Nanido da ke Karamar Hukumar Gassol a Jihar Taraba.

’Yan bindigar sun sace mai garin da matansa biyu ne a Kwantan Nanido a ranar Talata da dare, sannan suka je suka kashe wasu mutum hudu a kauyen Maigemu.

Rahotanni sun ce maharan, wadanda suka yi kaurin suna wajen addabar yankin Kogin Binuwai, wurin da hare-ahren da suke kaiwa a bisa babura ya tilasta masunta da manoman rani kaurace wa wajen neman abincinsu.

Shugaban yankin Mutumbiyu, Alkali Sani Muhammad (mai ritaya), ya bukaci karin jami’an tsaro a yankin don tabbatar da zaman lafiya da kare rayukan al’umma.

Ya shaida wa Aminiya cewa, ’yan banga na kokarin kare kauyukansu musamman a cikin dare, amma suna bukatar dauki daga sojoji.

Sai dai Kakakin ’Yan Sandan Jihar Taraba, DSP Usman Abdullahi, bai amsa wayar wakilinmu ba, ballantana a samu jin ta bakinsa game da faruwar lamarin.