✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

UAE ta dakatar da ba ’yan Najeriya bizar zuwa Dubai

Haramcin bizar zuwa Dubai ya shafi kowa a Najeriya

Hukumomin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) sun dakatar da bayar da biza ga ’yan Najeriya masu son zuwa Dubai.

Sanarwar hakan na kunshe ne a wata takarda da gwamnatin kasar ta aiko wa hukumomi Najeriya da kuma masu shirya tafiye-tafiye a ranar Juma’a.

A cewar Tribune, takardar ta fito karara ta bayyana cewa “ duk wata bukatar izinin zuwa Dubai ba za a karbe ta ba”.

Sananan ta kara da cewa, “Wannan kin bayar da izinin ya shafi kowa a Najeriya.”

Lafazin takardar na nufin hatta jami’an hukumomi da kuma gwamnati, ba za a ba su bizar ba, har sai nan da wani lokaci.

Ga wadanda suka mika tarkardun bukatarsu, suka kuma biya, ba za a mayar musu da kudadensu ba, a cewar rohoton.

Wannan hanin shi ne mataki da kasar UAE ta dauka na baya-bayan nan tsakaninta da Najeriya.

Kasar ba ta kuma bayar da dalilin daukar wannan mataki kan ’yan Najeriyar ba.