Shugaba Muhammadu Buhari ya gana da shugabannin jihar Benuwe a fadarsa da ke Abuja jiya kan hare-haren da aka kaiwa wasu al’ummomi kwanannan a jihar inda ya nemi su rungumi abokanen zamansu ’yan Najeriya.
A sanarwar da mai magana da yawunsa ya fitar, Mista Femi Adesina ya ce shugaban kasar ya yi kira ga shugabannin jihar su hana mutanensu daukar fansa.
Shugaba Buhari ya bayar da tabbacin cewa wadanda suka kitsa hare-haren a jihar za su fuskanci fushin hukuma.