✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda jiragen soji suka ragargaza sansanin ISWAP A Dajin Sambisa

An bi sahun ’yan ta’addan maboyarsu a cikin kungurmin jeji inda aka rika cilla musu bama-bamai ta sama.

Rundunar sojin Sama ta Najeriya ta kai farmaki kan sansanin kungiyar Boko Haram, inda ta kashe ’yan ta’adda da dama tare da lalata maboyarsu a vankin Parisu da ke gefen Dajin Sambisa a jihar Borno.

Harin da sashen sojin sama na Rundunar Operation HADIN KAI ya kai a ranar 5 ga Disamba, ya kashe mayakan ISWAP masu dimbin yawa.

Kafin nan sai da jirgin rundunar ya kai hari bayan samun sahihan bayanai kan abin da ke faruwa a wasu manyan sansanonin ’yan ta’addar inda ya hallaka mayaka masu yawan gaske.

Wata majiyar tsaro ta ce an bi sahun ’yan ta’addan ne zuwa maboyarsu a cikin kungurmin jeji inda aka rika cilla musu bama-bamai ta sama.

Hare-haren sun lalata ginin da ’yan ta’addan suke ciki da kuma kayan aikinsu yayin da wadanda suke yunkurin tserewa daga yankin kuma aka rika yi musu dauki dauki-dai-dai ta sama.