Mahara da ba a san ko su wane ne ba sun harbe wani mai gidan saukar baki na Falola Hotel da ke Ilesa a Jihar Osun har lahira.
A yammacin Alhamis ne Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Osun, Adie Undie ya tabbatar wa Aminiya aukuwar lamarin a garin Ilesa.
- ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda biyu sun sace matan aure
- Kada UNICEF ta yi mana shisshigi -Gwamnatin Kano
Ya ce rundunar ta fara bincike domin cafko ta kuma gurfanar da ’yan bingidar da suka harbe Mista Falola Oke a kusa da gidansa da ke Ilesa a ranar Laraba da yamma.
Ya ce, “Na bayar da umarnin a gudanar da bincike kan lamarin. Za a mayar da binciken zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Osogbo nan.
“Za a yi cikakken bincike kuma wadanda suka yi danyen aikin za su girbi abin da suka shuka”, inji shi.