Akalla ’yan sa-kai 63 ne aka tabbatar ’yan bindiga sun harbe a Jihar Kebbi.
Sashen Hausa na BBC ya rawaito cewa lamarin ya faru ne bayan ’yan sa-kan sun kaddamar da farautar ’yan bindigar a masarautar Zuru da ke Jihar.
- Shin daidaiton jinsi ne asalin abin da mata ke bukata?
- Rikicin Ukraine: Farashin gangar danyen mai zai iya kai wa $300 – Rasha
An dai harbe mutanen ne, wadanda tuni aka riga aka yi musu jana’iza, da sanyin safiyar Litinin.
Rahotanni sun ce ’yan bindigar dai sun buya ne a kan bishiyoyi, inda suka yi wa ’yan sa-kan kwanton-bauna.
Daga bisani dai sun bude wa ’yan sa-kan wuta bayan da suka riga suka gama yi musu kawanya.
Matasan da aka hallaka din dai sun fito ne daga kauyuka daban-daban na masarautar ta Zuru.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoton dai, hukumomin a Jihar ba su ce magantu ba a kan harin.