A ranar Asabar wasu masu tayar da kayar baya cikin ayarin motoci sun kai hari kan wani kauye da ke da ’yar gajeruwar tazara tsakaninsa da garin Askira Uba a jihar Borno.
Wani ganau ya shaida wa Aminiya cewa maharan da ake zargi mayakan Boko Haram ne dauke da bindigogi sun samu shiga kauye salin-alin cikin sauki da Yammacin Asabar.
- Dalibai 333 ne suka bace a GSSS Kankara —Masari
- An yi zanga-zangar neman a ceto daliban GSSS Kankara da aka sace
Mashaidin ya ce maharan sun shiga kauyen cikin azama kuma a gadarance ba tare da sun fuskanci wata tirjiya ta jami’an tsaro ba.
Aminiya ta ruwaito cewa masu tayar kayar bayan sun yi kiran Sallah da babbar murya bayan saukarsu a kauyen inji shaidar.
Sai dai akwai rahotanni masu cin karo da juna dangane da adadin wadanda suka rasa rayukansu da kuma rashin tabbas kan rahoton arcewar maharan.