✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaben 2023: Gwamnati ta bayar da umarnin rufe makarantun kimiyya da fasaha

Gwamnatin Tarayya ta bayar da hutun ne yayin da zaben 2023 ya karato.

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun Kimiyya da Fasaha ke fadin kasar nan, gabanin shiga zaben 2023.

Ministan Ilimi Adamu Adamu ne ya bayar da wannan umarni a wata takarda mai dauke da sa hannun wani jami’in ma’aikatar, I.O Folorunsho.

Wasikar wacce aka raba wa manema labarai a Abuja, an aika da ita ne zuwa ga Babban Sakataren Hukumar Kula da Ilimin Fasaha ta Kasa (NBTE), Idris Bugaje.

Ministan, ya bukaci a isar da wannan umarnin ga Shugabannin Makarantun Kimiyya da Fasaha domin dakatar da harkokin karatu daga ranar 22 ga Fabrairu zuwa 14 ga Maris, 2023.

Wasikar ta ce: “Saboda matsalolin tsaro da ka iya shafar ma’aikata, dalibai, da kuma dukiyoyi a cibiyoyinmu, Ministan Ilimi, Adamu Adamu, bayan tattaunawa mai zurfi da jami’an tsaro da abin ya shafa, ya umarci rufe dukkanin makarantun Kimiyya da Fasaha.

“Kuma za a dakatar da harkokin karatu daga ranar Laraba, 22 ga Fabrairu zuwa ranar Talata 14 ga watan Maris, 2023.”

Ana iya tuna cewa, a makon jiya ne Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta bayar da umarnin rufe jami’o’in kasar nan domin bai wa dalibai damar shiga zabukan da za a yi a ranakun 25 ga watan Fabrairu da 11 ga Maris.