✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zanga-zanga: Mutum 164 sun mutu a Kazakhstan

Zanga-zanga na ci gaba da tsamari sakamakon karin kudin man fetur da gwamnatin kasar ta yi.

Akalla mutum 164 ne aka kashe cikin mako daya a zanga-zanga a kasar Kazakhstan, kamar yadda Ma’aikatar Lafiyar kasar ta shaida wa manema labarai.

Kazalika, sama da mutum 2,200 ne suka ji rauni a yayin nuna adawa ga gwamnatin kasar a lokacin zanga-zangar.

A cewar ma’aikatar lafiyar, an duba mutum 719 da suka jikkata a ranar Lahadi, yayin da mutum 83 ke cikin mawuyacin hali.

Sai dai har yanzu mahukuntan gwamnatin kasar sun gaza tofa albarkacin bakinsu kan yadda zanga-zangar ke ci gaba da tsamari.

Zanga-zangar ta fara ne tun satin da ya gabata, inda dubban mutanen kasar ke nuna adawa ga hukuncin gwamnatin na kara farashin man fetur da ta yi.

Zanga-zangar ta jawo koma baya da kuma durkeshewar kasuwancin mutane da dama a kasar.

Sai dai rahoton wani gidan talabijin ya bayyana cewar a iya yankin Almaty, mutum 103 ne suka mutu, ciki har da kananan yara.

Amma baya-bayan nan hukumomi a kasar sun ce mutum 40 ne suka rasa rayukansu ciki har da jami’an soji da na ’yan sanda.

Sanarwa daga Fadar Shugaban Kasar, Kassym-Jomart Tokaye, ta ce gwamnatin na kokarin shawo kan zanga-zangar cikin lumana don kaucewa tashin-tashina da fada wa mummunan yanayi.