✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

2023: Ganduje ya ki amincewa da ajiye aikin Shugaban KAROTA

“Tabbas na mika wannan takarda amma Gwamna ya ce na dakata tukunna”

Shugaban Hukumar Kula da Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA), Baffa Babba Dan-Agundi, ya ce Gwamnan Jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya ki amincewa da bukatarsa ta ajiye aiki.

A kwanan nan ne dai Baffan ya aike wa Gwamnan takardar neman ajiye aikinsa don yin takara a zaben shekarar 2023 da ke tafe, kamar yadda Dokar Zabe ta tanada.

Sai dai da yake magana da wakilinmu, Shugaban na KAROTA ya tabbatar da cewa ya mika takardar ajiye aiki a ranar Litinin, amma hakarsa ba ta cim ma ruwa ba.

“Tabbas na mika wannan takarda amma Gwamna ya ce na dakata tukunna.

“Gwamna kamar uba yake a wajena, domin haka, ba zan bijirewa bukata ko umarninsa ba,” inji shi.

Ya kara da cewa shi mai biyayya ne ga umarnin Gwamnan a matsayinsa na wanda ya taimaka mishi wajen cim ma nasarori a rayuwa.

Tun farko dai sakamakon kin amincewa da takardar ajiye aikin ya fito ne ta hannun Mukaddashin Gwamnan Jihar, Nasiru Yusuf Gawuna, bisa umarnin Gwamna Ganduje a halin yanzu yake birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Ana ganin Baffa Babba Dan-Agundi dai a matsayin daya daga cikin na hannun daman Gwamna Ganduje a Kano.