Matar Shugaban Kasa, Aisha Buhari, ta janye karar dalibin nan da take zargi da cin mutuncinta a kafofin sada zumunta, Aminu Mohammed.
A ranar Juma’a, lauya mai gabatar da kara, Fidelis Ogbobe ya shaida wa kotun cewa Aisha Buhari ta janye karar ne bayan wasu ’yan Najeriya sun sanya baki.
- Wike da Ortom sun kalubanci Buhari ya fallasa gwamnonin da ke sace kudaden kananan hukumomi
- ‘An yi garkuwa’ da mutane a masallaci a Delta
Tsare dalibin da jami’an tsaro suka yi a makon jiya, kafin daga baya kotu ta tsare shi, ya janyo ce-ce-ku-ce da sukar matar shugaban kasar, gami da kira da a gaggauta sakin shi.
Idan ba a manta ba, Aminiya ta ruwaito yadda matar shugaban kasar ta rufe shafinta na Twitter a lokacin da aka yi mata ca kan tsare Aminu.