An kama wani dillalin makaman ’yan bindiga tare da wasu ’yan fashi a Jihar Zamfara.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Abutu Yaro ya ce an kama dillalin makaman ne suna cikin cinikin bindiga kirar AK-47 daga wani dan bindiga a daji.
- Zamfara: ’Yan bindiga sun yi wa mutane luguden wuta a kasuwa
- Mahara sun yi awon gaba da matar Dagaci a Kebbi
- Mutum 56 na kwance a asibiti bayan bullar wata bakuwar cuta a Kano
“Jami’anmu masu sintiri sun yi nasarar kama wani mutum da tsabar kudi Naira miliyan daya da dubu saba’in.
“A yayin da muka titsiye shi ne ya bayyana cewa an ba shi kudin ne ya kai wa wani a Karamar Hukumar Zurmi.
“Bisa hakan ne jami’anmu suka kama wani gawurtaccen dan ta’adda da bindiga kirar AK-47 da harsasai, ana kuma kokarin kamo abokan sana’ar tasu,’’ inji Kwamishinan ’Yan Sandan.