✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An dauki Jose Peseiro sabon kocin Super Eagles

Jose Mourinho ne ya ba Hukumar NFF din ta dauka a matsayin mai horar da ‘yan wasanta.

Hukumar Kwallon Kafar Najeriya NFF, ta sanar da daukar Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles.

Hukumar ta sanar da hakan bayan taronta na ranar Laraba.

A sanarwar, “bayan nazarin wasikar shugaban kwamitin tsare-tsare da ci gaban wannan hukumar, Kwamitin Zartarwa ya amince da zabar Mista Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles.

“Sai dai hukumar ta amince kocin wucin gadin tawagar wato Austin Eguavoen ya jagoranci kasar a gasar Kofin Afirka da za a fafata a Kamaru, shi kuma sabon kocin ya zama mai lura a gasar. Hakan zai sa su fara samun alakar aiki tare tun yanzu.

Jose Santos Peseiro tsohon dan kwallo ne mai shekara 61 da ya buga tamaula a matsayin dan wasan gaba.

Ya taba horar da kungiyoyin Sporting CP ta Portugal da FC Porto da Real Madrid a matsayin mataimakin koci, da tawagar kwallon kafa ta Saudi Arabia, sannan a karshe-karshen ya horar da kasar Venezuela, inda suka rabu a watan Agustan da ya wuce.

Dan asalin kasar Portugal ne wanda kocin AS Roma, Jose Mourinho ya ba Hukumar NFF din ta dauka a matsayin mai horar da ‘yan wasanta, inda har wasu rahotanni suka nuna cewa Mourinho din ya yi alkawain zai rako shi Najeriya ranar da za a gabatar da shi.