✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama masu hakar gwal ta barauniyar hanya a Zamfara

Mutanen sun ci gaba da hakar ma'adinai duk da haramcin da gwamnati ta sanya

Sashen ’yan sanda da ke yaki da masu hakar gwal ta barauniyar hanya a Jihar Zamfara ya cafke mutum 18 masu hakar gwal ta bayan fage duk da umarnin Shugaban Kasa na haramta ayyukan hakar gwal a yankin. 

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar, SP Shehu Mohammed ya sanar a ranar Juma’a a garin Gusau cewa Rundunar, karkashin jagorancin SP Murtala Bello, daga Abuja mai aikin sanya ido tare da tabbatar da umarnin na Shugaban Kasa a Jihar ne ta samu nasarar.

“Kamen masu hakar gwal ta barauniyar hanyar, an gabatar da shi ne a yankin ’Yan Kaura a Karamar Hukumar Maru, inda yawancin mazauna suke hakar gwal din ta bayan fage.

“Rundunar ta yi aikinta cikin nasara tare da cafke wadanda ake zargi da karya dokar su 18.

“Da zarar an kammala bincike za a gurfanar da su a gaban kotu don su girbi sakamakon abin da suka aikata,” a cewarsa.

Ya bayyana cewa an kama mutanen da ake zargin da kayayyakin laifi da dama da suka hada da jakar sinadarai daban-daban da ake amfani da su wurin hakar gwal, sai wata mota kirar Lexus Jeep da sauran kayayyaki.