✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi garkuwa da Dan Majalisar Dokokin Taraba

’Yan bindiga sun yi wa Barista Bashir dirar mikiya suna barin wuta sannan suka dauke shi

’Yan bindiga sun yi garkuwa da Dan Majalisa mai wakiltar Mazabar Nguroje a Majalisar Dokokin Jihar Taraba daga gidansa.

Masu garkuwa dauke da muggan makamai sun yi awon gaba da Barista Bashir Mohammed ne da misalin karfe 1.30 da daren Laraba daga gidansa da ke unguwar Yama Sala a garin Jalingo.

Shaidu sun ce kusan mutun 20 ne suka yi dirar mikiya a gidan dan majalisar suna barin wuta na kusan minti 45 kafin su tisa keyarsa ba tare da jami’an tsaro sun kawo dauki ba.

Makwabta sun shaida wa Aminiya cewa maharan sun shafe tsawon lokaci a gidan dan majalisar, har suka kamo shi da karfin tsiya a dakinsa suka sa shi a motarsu suka bar unguwar a sukwane.

Da yake tabbatar da aukwar lamarin, Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba, DSP David Misal, ya ce tun rundunar ta fara aiki don ceto dan majalisar.

Bashir Mohammed shi ne dan majalisan na biyu da ’yan bindiga suka yi garkuwa da shi a Jihar Taraba.

A shekarar 2017 ’yan bindiga sun sace wani Dan Majalisa Hosea lbi a gidansa da ke garin Takum kuma suka kashe shi bayan sun karbi miliyoyin Nairori a matsayin kudin fansa.