✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi jana’izar dan majalisar Kadunan da ’yan bindiga suka kashe

Daga cikin wadanda suka halarci jana'izar, har da Gwamna El-Rufa’i.

Dubban jama’a ne suka halaci jana’izar dan Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rilwanu Aminu Gadagau da ’yan bindiga suka kashe a ranar Talata.

Daga cikin wadanda suka halarta har da Gwamnan Jihar, Malam Nasiru Ahmed El-Rufa’i, tare da yan Majalisar Dokoki na Jihar.

A daren Litinin ne da misalin karfe 8:30 ne na ranar ’yan bindigar suka datse hanyar a daidai Dumbin Rauga, inda suka dauki tsawon lokaci suna kashe mutane.

Daga nan ne suka kwashe mutanan da ba a san yawansu ba cikin su har da marigayin.