Rahotanni daga karamar hukumar Bida a jihar Neja na bayyana cewa, mummunan hadurra biyu na motoci ya yi sanadiyyar rasuwar mutum 15 da raunata mutum 42.
Darakta Janar na hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar Neja NSEMA, Alhaji Ahmed Ibrahim Inga ya tabbatarwa majiyarmu aukuwar hadari.
A cewar Alhaji Ahmed, hadarin farkon ya faru tsakanin wata tirela dauke da shanu da ke tafiya a hanyar Minna zuwa Bida, yayin da dayan kuma hadarin ya faru da wata tirela da ta dauko tumatir a hanyar Bida zuwa Mokwa duk a cikin jihar.