✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Har yanzu kuna tare da mu —Martanin ECOWAS ga Nijar, Mali da B/Faso

Kasashen sun sanar da ficewarsu daga ECOWAS, amma kungiyar ta ce ba ta da labari

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ce kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso ba su sanar da ita ficewarsu daga cikinta a hukumance ba.

Kungiyar ta ce a shanun tashi ta ji labarin ficewar kasashen, tana yin iya kokarinta na ganin a daidaita al’amura a tsakaninsu.

Hakan dai ya biyo bayan janyewar dakarun soji daga kasashen da ECOWAS ta yi.

Kasashen sun sanar da ficewarsu daga ECOWAS a ranar Lahadi.

Kasashen uku, da ke yankin Sahel wadanda sojoji suka hambarar da gwamnatocin dimokuraiyya, sun dauki matakin ne a tare bayan zama da juna.

Wannan dai na dauke ne cikin wata sanarwa da kakakin mulkin sojin Nijar, Kanal Amadou Abdramane, ya fitar.

Sanarwar ta ce, “Al’ummar Burkina Faso, Mali, da Nijar na suna takaici cewa a tsawon shekaru 49 kungiyar ECOWAS ta bar turbar da aka gina ta a kai.

“Kungiyar ta gaza taimakon wadannan kasashe wajen yaki da ta’addanci da rashin tsaro.”

ECOWAS karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, ta yi barazanar daukar matakin soji idan har gwamnatin Nijar ta ki mika mulki ga farar hula a kasar.

Sai dai gwamnatin sojin Nijar ta ki aminta da sharadin da aka gindaya mata, yayin da kasashen Mali da Burkina Faso suka goya wa Nijar baya.

A ranar Lahadi ne dai, shugabannin kasashen yankin Sahel uku, suka dauki matakin ficewa daga kungiyar ECOWAS.

Tun da farko shugabannin ECOWAS, sun dakatar da kasashen uku bayan juyin mulkin da sojoji suka yi musu.